Shugaba Muhammadu Buhari zai yi hutun karshen mako a birnin Landan na kasar Ingila, Bayan kammala hutun kwanaki 10 da yaje yi a kasar.
Yayin hutun na sa Shugaba Buhari ya ga likita inda aka sake duba lafiyar kunnensa wanda aka yi masa magani Tun anan gida Najeriya.
A yammacin jiya ne dai Shugaba Buharin ya bayyana wa mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbajo wannan mataki ta wayar tarho.
Shugaba Buhari na cikin koshin lafiya sa6anin jita-jita da ke ta yawa a kafafen yada labarai na zamani, zai kuma kama aiki a ranar Litinin mai zuwa.
0 Response to "SHUGABA BUHARI ZAI DAWO GIDA NAJERIYA RANAR LAHADI"
Post a Comment