MASASSARAR NAJERIA TA HARBEMU

Bismillahi.. 
Wannan wani Rubutu ne dana taba yi a Jaridar Aminiya ta Ranar 20 ga watan Octoban 2013. Sabo da Muhimmancinsa ne ma naga ya dace na sake Rubutashi. Asha Karatu Lafiya.




Map of Nigeria
Tarihi shi ne rayuwa, fahimtarsa ko gane aukuwarsa ita ce gishirin rayuwar, aiki da abin da tarihin yazo dashi shine abincin rayuwar. Shi ya sa masana ma ke iya ikirarin duk wanda bai san abin da ya faru ba ( a gidansu, ko unguwa ko kauye ko sasa) kafin a haife shi, to tabbas bai san  tarihin rayuwarsa ba kuma haka zai kasance tamkar jariri, wato bai san komi game da rayuwa ba. Shi kuwa jariri ai mun san ba kawai rashin sanin abin da ya wakana ba ne ya dame shi, a’a jikinsa da wawalwarsa da yanayin ginuwar rayuwarsa.
Da sanin tarihi zaka iya gane wane ciki jiya ta samu, kuma me ta Haifa yau kuma da sanin tarihi zamu fahimci wane irin yara za’a samu gobe. Duk da yake shekaruna baza su wuce ashrin dawani abu  ba kuma bazan iya kiran kaina a matsayin tsarrar Nigeria ba kamar yadda Mahaifina zai kira. Kasancewa an haifi mahaifina ranar da Nigeria ta samu yancin kai kuma yana sanar dani abubuwa masu yawa da suka wanzu a zamaninsu. Mafi yawan lokaci idan yana bani labarin remon democradiya da suyka sha da yadda ake musu gata a lokacin da suke makaranta sai naji tamkar a wata kasa suka rayu. Na dade ina mamakin yanayin yadda suka gudanar da makarantarsu cikin jin dadi da kwanciyar hankali amman mu kuwa ko oho.

Image result for nigerian map
            Zan iya tunawa a jami’ar mu wani malami yana bamu labarin rayuwar da sukayi a lokacin suna kanana, daga lokacin haihuwarsu zuwa lokacin da aka musu kaciya. Ni kuma naka da baki nace da Malam “Jiya ba yau ba! Lallai Malam kun taso cikin mani'imciyar rayuwa kai da Nijeriya tsararka. Mu kuwa da muka tsiro a daidai lokacin da Nijeriyar ta fara kamuwa da masassara (1985-1995), masassarar ta harbe mu. Domin kuwa abin da zan iya tunawa shi ne a daidai lokacin da aka yi mana kaciyar, garinmu babu asibitin da likita zai mana shayi, ballantana wani abu wai shi da wutan lantarki ko ruwan famfo. A gida aka giggille mu da askar wanzami tamkar yadda aka yi wa kakanninmu. Mun dai dan ci kajin ba laifi; maganar lantarki da asibiti kuwa ma iya cewa jiya i yau. Bambancin kawai bai wuce turakun da aka kakkafa mana daure da wayoyi ba, hasken kuma sai mako-mako kamar sauran yankunan karkara takwarorin namu. Haka batun yake ga ginin asibiti, amma kiwata lafiyar sai mai Naira. Ruwan famfo kuwa sai in mun yi katarin shiga birni daidai lokacin da yake kwarara.To, muna fata dai Allah ya warkar da Nijeriya daga wannan masassara da take fama da ita. Idan kuma ciwon ajali ne, to Allah ya yi mata kyakkyawar cikawa. Malam kuma Allah ya kara tsawon rai amin!”
            Haka malamin nan yayi murmushi yace: “Malam Mujahidu kenan. Hakuri za kuyi don wannan kasar sai addu’a don Kullum abubuwan kara lalacewa yakeyi.”

A shugabancin baya an gina zuciyoyin yan Nigerai ne a matsayin mutanen da zasu taso su gina kasa, suyi komai ba don amfanin kansu ba sai don amfanin alummmar kasar nan. Koda yake nima zan iya cewa  malaman firamaren mu sun ginamu da wannan tarbiyar. Don wajajen 1996 zuwa 2000 lokacin ina ajin farko zuwa aji hudu na makarantar firamare malaman mu sunyi kokari matuka don suga mun tarbiyantu wajen son al’umma da gina kasa.
A wannan lokaci idan an tambayemu me muke son mu zama sai kaji kowa na fadan ra’ayinsa. Kamar ni a lokacin ina cewa ne ina son na zama Likita mai taimakama al’umma. Wani kaji yace yana son ya zama Dan Sanda mai kare Kasa, Malami mai horror da dalibai ko kuma Dan Jarida maii taimakon Al’ummma. Haka dai kowa ke fadan ra’ayinsa kuma a lokacin kowa burinsa kenan amman sai kasha cikin kankanin lokaci tunaninmu ya sauya. A kwanakin baya na samu wasu yara yan makarantar firamare nake tambayarsu me suke so su zama nan gaba. Sai daya yayi sauri yace shi yana son ya zama shuganan kasa ne, wani kuma yace gwamna.
            Ya salam! To ya akayi cikin kankanin lokaci tunanin kowa ya sauwa. Abin ba’a yara kawai ya tsaya ba. Mu kanmu yanzu mafiyawan ‘yan ajinmu munje muna karatu a inda mukasan zamu samu kudi da yawa. Mafi yawa daga cikin mu basa tunanin kudin ta wace hanya zai fit aba. Hallas ko haram.
            Abuwa masu dadi sun  faru lokacin da Nigeria take da shugabanni maso kishinta. Wutan Nepa, kiwon lafiya, makarantu, walwalan jama’a da sauransu. Amman mu a zamaninmu mun samu akasin haka. Idan kace zakayi makaranta to akwai yajin aiki, idan kasuwanci ne to kasa ba tsaro. Haka batun yake ga wadanda suka gama karatun don babu aikin yi. To yanzu me ake son dan kasar nan yayi. Idan kayi Magana ace baka da kunya, idan kayi shiru ace bakasan yancin kanka ba. Idan kayi zabe baka ganin abin daka zaba sai abin da manyan mu suka zabar mana.
            Matsalolin haka suke faruwa karuwa kullum. Amman a kowane haquri akwai nasara amman duk alummar data manta Allah dole Allah ya manta da ita. Kowa zai iya gina rayuwarsa a inda yake ganin ya dace dashi amman mafi kyawun rayuwa shine rayuwa da tsoron Allah. Muyi ma kanmu guzuri don mafi kyawun guzuri shine Imani. Allah ya tsare kasarmu da mutanan cikinta.

Alhamdulillahi...

1 Response to "MASASSARAR NAJERIA TA HARBEMU"